News
Tirela Ta Kashe Mutum 6 Wasu 15 Sun Ji Rauni A Jihar Gombe
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Mutane 6 sun mutu wasu 15 suka ji raunuka a wani hatsarin da wata tirela ta yi a hanyar Abacha Raod da ke unguwar Jekadafari a garin Gombe.
Kwamandan Hukumar Kiyaye Haddura ta Ƙasa a jihar Gombe, Felix Theman ne ya tabbatar da hakan a yammacin ranar Juma’a.
Ya ce tirelar tana dauke ne da shanu 27 da wasu yara a saman bodin ta.
Ya ce hanyar ta yi kadan wa manyan motoci su bi, amma masu tireloli suna kaunar bin ta, duk da cewa tana da kwane-kwane.
Aminiya ta ruwaito cewa Ya ce irin Yyran da suke hawan saman bodin motar sune suke yin ihu suna zuga direbobin su kuma suke kara gudu a cikin gari saboda burgewa da hakan ya kai su ga hatsari.
Daga nan sai ya ce za sun yi zama da masu ruwa da tsaki a harkar tukin manyan motoci dan jan kunnen direbobin tirelar da mafi yawan lokaci suke bai wa yaran motarsu suke ganganci a cikin gari domin kiyaye yawan aukuwar hatsari.
-
News2 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
