News
Dukkan MDs ya kamata su bi sahun Manajan Darakta na Hukumar Yawon shakatawa wajan inganta ma’aikatansu – Mataimakin Gwamnan Jihar Kano
DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA
Mataimakin gwamnan ya bayyana jin dadinsa ta yadda manajan daraktan ya yi kokarin gyara hukumar tare da inganta kwarewar ma’aikatansa, inda ya ce hukumar yawon bude ido muhimmin bangare ne na al’umma da al’adu.
Ya bayyana haka ne a lokacin kaddamar da ayyukan gyare-gyare a hukumar kula da yawon bude ido ta jihar Kano da aka gudanar kwanan nan.
Hakan na kunshe ne ta cikin wata Sanarwa da jami in yada labarai na Hukumar yawon bude ido ta jihar Kano Abdulbasit Bello Sani ya turawa da Jaridar Inda Ranka
Sanarwa ta kara da cewa Muhimmancin yawon bude ido a tsakanin al’umma shi ya sa muka tattaro manyan jami’an gwamnati da suka hada da kwamishinonin sufuri, sa ido da tantancewa, kudi, kasuwanci da masana’antu da ayyuka na musamman. Haka kuma a cikin tawagar akwai Babban Sakatare, Ofishin Tarihi & Al’adu, Manajan Darakta ARTV da Manajan Daraktan Hukumar Kula da Dabbobi na Kano. Don haka ina kira ga MDA; s da su yi koyi da kyakkyawan aikin hukumar yawon shakatawa wajen inganta da kuma kula da tsaftataccen muhalli
Gwarzo ya bukaci al’ummar jihar Kano da su koma kan muhimman al’adunsu na mutunci tare da baiwa gwamnati hadin kai wajen kiyaye dimbin al’adunmu.
Al’adarmu ita ce madubin rayuwarmu da ke jan hankalin ‘yan yawon bude ido zuwa garinmu. Don haka guje wa al’adunmu da ruguza abubuwan tarihinmu shi ne ke tabbatar da lalacewar tattalin arzikinmu da kimarmu.”
Ya kuma isar da sakon gwamnan cewa ya yi farin ciki da jajircewar hukumar da ma’aikatan hukumar. Ya yi fatan za su ci gaba da yin aiki tare da manajan darakta da gwamnatin jihar baki daya.
Tun da farko dai shugaban hukumar yawon bude ido ya nuna jin dadinsa ga yadda mataimakin gwamnan ya amince da gudanar da ayyukan duk kuwa da takurewar da ya yi.
Bugu da kari, yana mika godiya da godiya ga kokarin da gwamnan ya yi ta hanyar ba da amincewar sake fasalin cikin kankanin lokaci.
-
News2 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
