News
Da Dumi-Dumi: Abba Gida-gida Ya Nada Kwankwaso, Ganduje, Shekarau, Mukami A Kano
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Gwamnan Jihar Kano Yusuf Ya Nada Kwankwaso, Shekarau , Ganduje Mukami A Kano
Gwamna Yusuf ya bayyana hakan a Abuja ranar Asabar yayin da yake jawabi ga manema labarai .
Mutum Miliyan 9.19 Ne Ke Da Lambar Katin Dan Kasa Ta NIN A Jihar Kano – NIMC
A cewar gwamnan, majalisar za ta yi aiki a matsayin hukumar ba da shawara ga gwamnatin jihar .
SOLACEBASE ta ruwaito cewa mambobin majalisar sun hada da gwamnoni da mataimakansu da suka shude, shuwagabannin majalisar jiha da mataimakansu, shugaban majalisar dattawa da mataimakinsa (Idan akwai), alkalai masu ritaya, CJN mai ritaya (Idan akwai), Alkalan kotun koli da suka yi ritaya, alkalan kotun daukaka kara da Musulunci da suka yi ritaya. shugabanni, da sauransu.
Da wannan ne Rabiu Musa Kwankwaso, Ibrahim Shekarau, da Abdullahi Umar Ganduje ke zama mambobin majalisar.
Gwamnan ya jaddada kudirin sa na ci gaba da gudanar da gwamnati a bude domin tafiya da kowa da kowa.
