Connect with us

News

Tinubu ya aikewa majalisar kasar nan kudirin mafi Karancin albashi na naira 70k

Published

on

DAGA KABIR BASIRU FULATAN 

 

Shugaban Kada Bola Ahmad Tinubu ya bukaci majalisar dokokin kasar nan da ta amince da kudirin biyan mafi karancin albashi na N70k

Tinubu ya bukaci majalisar dokokin kasar da ta amince da kudurin dokar mafi karancin albashi ya zama dokar da za,a Fara aiki da ita

Bukatun Hakan na kunshe ne a cikin wasikun da aka aike zuwa ga shugabannin majalisun guda biya tsakanin majalisar dattawa data wakilai

Tajudeen Abbas shine kakakin majalisar ya karanta wasikar da Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, yayin zaman majalisar a ranar Talata.

Advertisement

Kudirin ya bukaci a tsara mafi karancin albashi na N70,000 da gwamnatin tarayya ta amince da shi kwanan nan da kungiyoyin kwadago.

Idan za,a iya tunawa jaridar inda ranka ta rawaito cewa Hakan na zuwa ne daidai lokacin da aka cimma matsaya a ysakanin kungiyoyin kwadago ta TUC da NLC da Kuma gwamnatin tarayya

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending