Connect with us

News

Kamfanin NNPCL Ta Fitar Da Farashin Yadda Kowacce Jiha Zata Sayi Man Matatar Dangote

Published

on

download (3)

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

Kamfanin mai na Nijeriya NNPCL ya fitar da sabon farashin da za a rinƙa sayar da man fetur a ƙasar bayan ya fara karɓar fetur ɗin daga matatar Dangote a ranar Lahadi.

Advertisement

Kamfanin ya sanar da farashin ne a wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin da safe.

Hukumar DSS ta saki Omoyele Sowore Shugaban Jaridar Sahara Reporters

NNPCL ɗin ya bayyana cewa a Jihar Borno da kewaye za a sayar da fetur ɗin har kan N1,019 kan kowace lita sai kuma Kaduna da Sokoto da Kano da wasu jihohin za a sayar da fetur ɗin kan N999.22.

Advertisement

Sai kuma Abuja babban birnin ƙasar za a sayar da fetur ɗin kan 992.2

Sai kuma jihar 0yo kan N960 sai Ribas 980 kan N960 kan kowace lita.

Advertisement

A cewar NNPCL, a Jihar Legas ne za a fi sayar da fetur ɗin a farashi mai rahusa inda za a rinƙa sayar da shi kan N950.22 kan kowace lita.

Kamfanin na NNPCL ya tabbatar da cewa a wannan watan na Satumba zai biya kamfanin Dangote da dala domin ɗaukar man fetur, inda ya ce a ranar 1 ga watan Oktoba ne zai soma biya da naira.

Advertisement

Kamfanin na NNPC ya bayar da tabbacin cewa idan aka samu sabani game da farashin da aka yanke, za yi matuƙar godiya ga duk wani rangwamen da matatar Dangote za ta yi, wanda rangwamen zai je ga jama’a kai tsaye.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending