Connect with us

News

Shugaban Tinubu Ya Gana Da Firai Ministan India Narendra Modi A Fadarsa Dake Abuja

Published

on

FB IMG 1731866337352

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Shugaban Kasa Bola Tinubu ya gana da Firai Ministan India Narendra Modi a fadarsa dake Villa babbban birnin Tarayya Abuja a yau lahadi.

Jaridar Daily Trust ta rawaito a jiya Asabar ce Firai Ministan India Narendra Modi ya iso Nageriya a ziyarar da ya kawo domin kara kulla alaka mai karfi a tsakanin Kasashen biyu.

Advertisement

Haka zalika Shugaban Tinubu Ya jinjinawa Narendra Modi inda ya bashi , lambar girmamawa ta Najeriya mafi alfarma ta GCON. Inda shugaban ya ce Hakan alama ce ta yabo da jajircewar Najeriya.

 

Advertisement

A kawancen da Najeriya da kasar Indiya suka kulla Kasashen sun jaddada aniyar gina kwakkwarar alaka, inda suka sha alwashin karfafa dangantaka a muhimman fannoni irinsu bunkasa tattalin arziki da tsaro da kiwon lafiya da kuma samun wadatar abinci.

A yayin tattaunawar tasu, shugabannin 2 sun amince da samun karin hadin gwiwa a fannin yaki da ta’addanci da tsaron teku da kuma musayar bayanan sirri.

Advertisement

Ratotannin na nuni da cewa wannnan shine Karo na farko da Firai ministan India ya kawo ziyarar Najeriya tun bayan , ziyarar da karamin firai minista Dr Manmohan Singh ya kawo a shekara ta 2007, lokacin da kasashen biyu suka kulla kawance mai inganci.

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending