Connect with us

News

Da Dumi Dumi : Gwamnan Kano Ya Naɗa Umar Faruk Ibrahim A Matsayin Sabon Sakateran Gwamnati 

Published

on

1739051589975

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya nada Umar Farouk Ibrahim a matsayin sabon sakataren gwamnatin jihar Kano wato (SSG).

Advertisement

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa jaridar Inda ranka a ranar Asabar.

Sanarwar ta ce nadin Ibrahim zata fara aiki daga ranar Litinin 10 ga Fabrairu, 2025 bayen maye gurbinsa da tsohon sakataren gwamnatin Alhaji Baffa Bichi.

Advertisement

Haka zalika Sanarwar ta ce, an zabi Ibrahim ne bisa gogewar da yake da ita, wanda ake sa ran zai yi amfani da ita wajen inganta harkokin gwamnatin jihar Kano.

 

Advertisement

Umar Farouk Ibrahim dai ya kwashe sama da shekaru talatin yana aikin gwamnati , don haka ake fatan zai kawo cigaba sosai a sha’anin tafiyar da harkokin aikin gwamnati.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending