Connect with us

News

SERAP Tayi Karar NNPC Kan zargin wawure Naira biliyan 825 Da Dala Biliyan 2.5

Published

on

Kungiyar SERAP ta kai ƙarar NNPCL bisa zargin batar da makudan kuɗaɗen da aka ware don gyaran matatun mai, tare da gargaɗin cewa hakan na haifar da talauci da koma baya ga tattalin arziki.

An shigar da ƙarar ne a Babbar Kotun Tarayya da ke Legas, bisa rahoton babban mai binciken kuɗi na Ƙasa na shekarar 2021, wanda aka fitar a watan Nuwamba 2024.

Advertisement

An Sanya Dokar Hana Zirga-zirga A Adamawa

Rahoton ya nuna akwai yiyuwar an batar ko an karkatar da kuɗaɗen da aka ware don muhimman ayyukan masana’antun man fetur na ƙasar nan.

SERAP ta ce maganganun attajiri Aliko Dangote da suka nuna cewa matatun man Najeriya na iya daina aiki gaba ɗaya, duk da biliyoyin dalolin da aka kashe wajen cewa ana gyara su, ya ƙara tabbatar da rashin gaskiya a harkar gyaran Matatun.

Advertisement

Kungiyar ta ce rashin bincike da dawo da waɗannan kuɗaɗe yana janyo talauci da koma baya ga tattalin arzikin ƙasa, tare da wargaza yunkurin wanzar da gaskiya da riƙon amana a fannin man fetur.

 

Advertisement

 

SAHARA REPORTS 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending