News
Shugaba Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Maiduguri Zuwa Muhammadu Buhari University
Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya sanar da sauya sunan Jami’ar Maiduguri da ke jihar Borno zuwa Jami’ar Muhammadu Buhari.
Shugaba Tinubu ya bayyana haka ne a wani taro na musamman na Majalisar Zartaswa ta Ƙasa da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja a ranar Alhamis.
KAROTA Ta Cafke Direban Da Ya Lalata Shuke-shuken Gwamnati A Kano
Taron, wanda ya kasance wani ɓangare na bikin tunawa da irin rawar da tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya taka wajen shugabancin ƙasar, ya gudana tare da halartar manyan jami’an gwamnati.
PRIME TIMES ta ruwaito cewa wannan sauyin suna yana cikin jerin matakan da gwamnatin Tinubu ke ɗauka domin girmama tsohon shugaban, wanda ya shugabanci Najeriya daga shekarar 2015 zuwa 2023.
Advertisements
