Connect with us

News

Shugaba Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Maiduguri Zuwa Muhammadu Buhari University

Published

on

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya sanar da sauya sunan Jami’ar Maiduguri da ke jihar Borno zuwa Jami’ar Muhammadu Buhari.

Shugaba Tinubu ya bayyana haka ne a wani taro na musamman na Majalisar Zartaswa ta Ƙasa da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja a ranar Alhamis.

Advertisement

KAROTA Ta Cafke Direban Da Ya Lalata Shuke-shuken Gwamnati A Kano

Taron, wanda ya kasance wani ɓangare na bikin tunawa da irin rawar da tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya taka wajen shugabancin ƙasar, ya gudana tare da halartar manyan jami’an gwamnati.

PRIME TIMES ta ruwaito cewa wannan sauyin suna yana cikin jerin matakan da gwamnatin Tinubu ke ɗauka domin girmama tsohon shugaban, wanda ya shugabanci Najeriya daga shekarar 2015 zuwa 2023.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending