Opinion
FARASHIN AMINCI DA GASKIYA: Dalilin Da Yasa Kyakkyawan Aikin Mustapha Muhammad Ya Wuce Yabo
DAGA ABDULKARIM IBRAHIM
A daidai lokacin da ake yawan jin rahotannin almundahana da karkatar da dukiyar jama’a daga wasu masu rike da mukaman gwamnati, wani mataki na gaskiya da rikon amana daga Jihar Kano ya jawo hankalin jama’a tare da sake tabbatar da cewa har yanzu akwai masu kishin amana a cikin masu gwamnati.
Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamnan Jihar Kano, Malam Mustapha Muhammad, ya samu yabo daga jama’a bayan ya mayar da Riyal 6,000 na Saudiyya, kwatankwacin kusan Naira miliyan 2.4, da aka yi masa kuskuren biyansa yayin rabon alawus-alawus ga ‘yan jaridar da suka halarci aikin Hajjin 2026 a Kasar Saudiyya.
ZAƁEN 2027: Bayan Shugaba Tinubu ƴan Takarar Shugaban Ƙasa 7 Ne Suka Fito Daga Kudancin Najeriya
Rahotanni sun nuna cewa kuskuren gudanarwa ne ya haifar da tura masa kudin da suka zarce adadin da ya kamata ya karba. Sai dai da zarar ya gano lamarin, ya sanar da masu ruwa da tsaki tare da mayar da kudin domin a gyara bayanan biyan kudaden da kuma tabbatar da cewa wadanda abin ya shafa sun samu hakkokinsu.
Ko da yake adadin kudin ba karami ba ne, abin da ya fi jan hankali shi ne yadda ya zabi gaskiya maimakon amfana da kuskuren da ba shi ne ya haddasa ba. Wannan mataki ya zo ne a lokacin da ake nuna damuwa kan raguwar kyawawan dabi’u da rikon amana a tsakanin wasu ma’aikatan gwamnati da masu rike da amanar jama’a.
Mutanen da suka san Mustapha Muhammad tun daga lokacin karatunsa a jami’a sun bayyana cewa wannan hali ba sabon abu ba ne a gare shi. Sun ce ya dade yana nuna jajircewa, biyayya ga ka’idoji da kuma gujewa duk wata hanya da za ta iya kawo masa nasara ba bisa gaskiya ba.
Haka zalika, wadanda suka yi aiki tare da shi a kafafen yada labarai na cikin gida da na kasa da kasa sun shaida irin mutunci, kwarewa da rikon amanar da ya nuna tsawon shekarun aikinsa.
Masana harkokin shugabanci sun bayyana cewa ainihin mutuncin mutum yana bayyana ne lokacin da ya samu damar aikata abin da bai dace ba ba tare da an gano shi ba, amma ya zabi bin hanyar gaskiya. A cewarsu, irin wannan hali na taimakawa wajen gina amincewar jama’a ga gwamnati da kuma karfafa nagartaccen shugabanci.
A nasa bangaren, Amirul Hajj na Jihar Kano kuma Sarkin Gaya, Alhaji Aliyu Ibrahim Abdulkadir, ya yaba da matakin da Mustapha Muhammad ya dauka, yana mai cewa hakan ya nuna gaskiya, adalci da daukar nauyin amanar da aka dora masa.
Masu sharhi kan harkokin gwamnati sun ce irin wadannan ayyuka sun cancanci a yaba musu domin karfafa kyawawan dabi’u a tsakanin ma’aikatan gwamnati. Sun ce ko da ba a bayar da kyautar kudi ba, karramawa a bainar jama’a ko takardar yabo na iya zama wata hanya ta zaburar da sauran ma’aikata su rungumi gaskiya da rikon amana.
Wannan lamari ya zarce batun Riyal 6,000 ko Naira miliyan 2.4 kadai. Labari ne da ke nuna muhimmancin mutunci, rikon amana da kuma zabar abin da ya dace a lokacin da mutum yake da damar yin akasin haka.
A lokacin da ‘yan Najeriya ke kira ga shugabanni da jami’an gwamnati masu gaskiya, matakin da Mustapha Muhammad ya dauka ya sake nuna cewa har yanzu akwai masu kishin amana a cikin hidimar jama’a, wadanda ke taimakawa wajen gina amincewar jama’a da kuma karfafa kyakkyawan shugabanci a kasa.
