News
An Gurfanar Da Jami’an ’Yan Sanda Biyar Bisa Zargin Hallaka Wani Mawaki
Babbar Kotun Jihar Delta da ke zamanta a Asaba an gurfanar da wasu jami’an ’yan sanda biyar da ake zargi da hannu a mutuwar Wani matashin mawaki Oghenemine Ogidi, wanda aka fi sani da OG Millan.
Jami’an da ake tuhuma sun hada da ASP Usman Nuhu, ASP Onoloko Dauroupamo, ASP Okoh Kelechi, Sufeto Goodluck Kingsley da Sufeto Omonigho Ahweyevu.
Mahara Sun Kashe ’Yan Yawon Sallah Bakwai A Sakkwato
An gabatar da karar ne a gaban Mai Shari’a Marshal Onome Umukoro na Babbar5Kotun Babbar Jiha mai lamba ta 5, karkashin shari’a mai lamba THC/ASB/CR/M/66C/2026.
Kotun ta bayar da umarnin tsare wadanda ake zargin a gidan gyaran hali na Ogwashi-Uku tare da dage sauraron karar zuwa ranar 15 ga Yuni, 2026.
Advertisements
