Connect with us

News

Gwamnatin Kano Ta Musanta Rahoton Alƙaluma Kan Yawan Jama’a, Masana’antu da Masallatai

Published

on

Hukumar Ƙididdiga ta Jihar Kano (KSBS) ta musanta wani rahoto da ke yawo a kafafen sada zumunta da wasu shafukan intanet, wanda ya ƙunshi alkaluma kan yawan al’ummar jihar, masana’antu, masallatai, coci-coci da kuma adadin yara marasa iyaye da ake zargin suna yawo a titunan Kano.

A cikin wata sanarwa da Darakta Janar na hukumar, Dakta Suraj Sulaiman, ya fitar, ya bayyana cewa rahoton da aka danganta da wani Garba Adamu, wanda wani shafin yanar gizo mai suna The Sultan of Hausa-Land ya wallafa, ba ya ɗauke da sahihan bayanan da Hukumar Ƙididdiga ta Jihar Kano ta fitar.

Gwamna Abba Ya Ayyana Murtala Sule Garo A Matsayin Wanda Zai Yi Masa Takarar Mataimakin Gwamna A Zaɓen 2027

Hukumar ta ce rahoton ya yi amfani da alkaluma marasa inganci, tare da bayyana cewa adadin masana’antun da ke aiki a Jihar Kano, waɗanda suka haɗa da ƙanana, matsakaita da manyan masana’antu, ya kai 3,632, ba 58 kamar yadda rahoton ya bayyana ba.

Haka kuma, KSBS ta ƙaryata ikirarin cewa Kano na da masallatai 435,389, tana mai cewa bayanan hukuma sun nuna akwai masallatan Juma’a 2,333 da aka tantance.

Dangane da ikirarin cewa akwai yara marasa iyaye miliyan 3.67 da ke yawo a titunan Kano, hukumar ta bayyana adadin a matsayin ƙarya, mai cike da ƙarin gishiri kuma ba shi da tushe a sahihan bayanan ƙididdiga.

Advertisement

KSBS ta buƙaci waɗanda suka wallafa ko suka yada rahoton da su gaggauta janye shi tare da bai wa al’umma haƙuri saboda yaɗa bayanan da ba su da inganci.

Hukumar ta sake jaddada cewa ita ce kaɗai cibiyar gwamnati da ke da hurumin tattarawa, tantancewa da fitar da sahihan alkaluman ƙididdiga na Jihar Kano, tare da kira ga jama’a da kafafen yaɗa labarai da su riƙa tantance sahihancin bayanai kafin wallafawa ko yaɗa su.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending