News
Nnamdi Kanu ya kalubalanci shari’ar sirri da ake masa
Daga Hamza yusif Abdulmumin
Jagoran kungiyar ‘yan aware ta IPOB a kudu maso gabashin Najeriya ya shigar da kara a watan kotun tarayyar kasar yana neman ta soke wani umarni da bangaren shari’a ya fitar a farko wannan watan da ke cewa za a daina sauraren dukkan shari’u na ta’addanci a bainar jama’a.
Nnamdi Kanu ya sanar da kotun ta hanyar lauyoyinsa cewa umarnin ya taka tsarin mulki da wasu dokokin kasar kuma ya kamata ta soke shi.
A ranar 8 ga watan nan ne mai shari’a John Terhemba Tsoho ya bayar da umarnin daina sauraren shari’un da ke da alaka da ta’addanci a bainar jama’a domin kiyaye tsaron dukan wadanda ke da alaka da shari’ar.
Alkalin ya hana ‘yan jarida halartar zaman kotunan da ke sauraren irin wadannan shari’un.
Baya ga alkalin da zai saurari shari’ar, mutanen da aka amince musu shiga dakin shari’ar su hada da wasu zababbun ma’aikatan kotun da jami’an tsaro.
Mista Kanu ya musanta aikata wani lifi.
-
News3 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
