News
Ƴan Boko Haram sun ɗauke mata 2 a Monduga — Kwamishinan Ƴan Sanda
Daga kabiru basiru fulatan
Kwamishinan Ƴan Sanda ns jihar Borno, Abdu Umar ya ce ƴan ƙungiyar Boko Haram sun sace wasu mata biyu a ƙauyen Mairari da ke Ƙaramar Hukumar Konduga.
Cikin wata uku an shigar da madarar naira biliyan 27 cikin Najeriya
Umar ya bayyana haka ne a wata hira da Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa, NAN a Maiduguri, inda ya ce lamarin ya faru ne a ranar 7 ga watan Yuni.
“Da misalin karfe 7:30, wani Ari Mustapha na kauyen Mairari a Konduga, ya bayar da rahoton cewa wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton mayakan Boko Haram ne sun mamaye gidansa tare da yin garkuwa da ‘ya’yansa mata guda biyu.
“Ya ce suna da shekarunsu 26 da 30.
“Ya kuma ce maharan sun sace bijiman sa guda biyu da wasu kayayyaki kafin su gudu,” in ji kwamishinan.
Kwamishinan ƴan sandan ya ce da samun bayanan, an tura tawagar ƴan sanda domin gano inda wadanda a ka sace su ke domin ceto su a kewayen wajen amma abin ya ci tura.
Umar ya ce rundunar za ta kara zage damtse har sai an ceto wadanda lamarin ya rutsa da su tare da sada su da iyalansu.
Kwamishinan ya bukaci jama’a da su riƙa kai rahoto ga jami’an tsaro na kusa da su.
-
News3 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
