News
Buhari na ganawar sirri da gwamnonin APC kan wanda zai yi wa Tinubu mataimaki
Daga Khadija Abdullahi Mahmud
Shugaban Ƙasa asa Muhammadu Buhari na ganawar sirri da wasu gwamnonin jam’iyyar APC mai mulki a fadar shugaban kasa ta Aso Rock Villa da ke Abuja.
Kotu ta ɗaure mutum biyu da ake yi wa shari’a tare da Abba Kyari
Gwamnonin sun samu jagorancin Shugaban kungiyar Gwamnonin APC, PGF, Gwamna Atiku Bagudu na Jihar Kebbi.
Waɗanda suka halarci ganawar sun haɗa da shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Farfesa Ibrahim Gambari; Sakataren gwamnatin tarayya, SGF, Boss Mustapha; Gwamna Babagana Zulum na Borno da Nasir El-Rufai na Kaduna.
Sauran sun haɗa da Gwamna Mohammed Badaru Abubakar na Jigawa; Abdullahi Sule na Nasarawa; Simon Lalong na Filato; Yahaya Bello na Kogi da Hope Uzodinma na jihar Imo.
Duk da dai ba a bayyanawa manema labarai maƙasudin taron ba, DAILY NIGERIAN ta tattaro cewa ganawar ba za ta rasa nasaba da yunƙurin zaɓar wanda zai yi wa ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu ba mataimaki.
Idan ba a manta ba, Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC ta bayyana cewa ranar 17 ga watan Yuni ne wa’adin mika sunayen ‘yan takarar shugaban kasa da mataimakan su zai ƙare.
-
News3 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
