Connect with us

News

Buhari na ganawar sirri da gwamnonin APC kan wanda zai yi wa Tinubu mataimaki

Published

on

Daga Khadija Abdullahi Mahmud

 

 

 

Shugaban Ƙasa asa Muhammadu Buhari na ganawar sirri da wasu gwamnonin jam’iyyar APC mai mulki a fadar shugaban kasa ta Aso Rock Villa da ke Abuja.

Kotu ta ɗaure mutum biyu da ake yi wa shari’a tare da Abba Kyari

Advertisement

Gwamnonin sun samu jagorancin Shugaban kungiyar Gwamnonin APC, PGF, Gwamna Atiku Bagudu na Jihar Kebbi.

Waɗanda suka halarci ganawar sun haɗa da shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Farfesa Ibrahim Gambari; Sakataren gwamnatin tarayya, SGF, Boss Mustapha; Gwamna Babagana Zulum na Borno da Nasir El-Rufai na Kaduna.

Sauran sun haɗa da Gwamna Mohammed Badaru Abubakar na Jigawa; Abdullahi Sule na Nasarawa; Simon Lalong na Filato; Yahaya Bello na Kogi da Hope Uzodinma na jihar Imo.

Duk da dai ba a bayyanawa manema labarai maƙasudin taron ba, DAILY NIGERIAN ta tattaro cewa ganawar ba za ta rasa nasaba da yunƙurin zaɓar wanda zai yi wa ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu ba mataimaki.

Idan ba a manta ba, Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC ta bayyana cewa ranar 17 ga watan Yuni ne wa’adin mika sunayen ‘yan takarar shugaban kasa da mataimakan su zai ƙare.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending