News
Ma’aikatan majalisa a Najeriya sun janye yajin aiki
Daga maryam bashir musa
Kungiyar ma’aikatan majalisar tarayya a Najeriya ta janye yajin aikin da ta shiga.
Buhari na ganawar sirri da gwamnonin APC kan wanda zai yi wa Tinubu mataimaki
Ma’aikatan sun shiga yajin aikin sai yadda hali ya yi a ranar Litinin ta makon da ya gabata, don matsa lamba na a biya su kudin alawus da suke bi.
Jaridun cikin gida sun ambato Shugaban na PASAN Sunday Sabiyi yana cewa sun aminta da janye yajin aikin ne bayan cimma wata matsaya da Shugabannin majalisar.
Sai dai PASAN ta yi barazanar sake tsunduma wani yajin aikin, matsawar Shugabancin majalisar ya gaza aiwatar da abinda suka cimma daga nan zuwa karshen Yuli.
-
News3 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News3 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
