Connect with us

News

Ba mu da masaniyar zama da ministan kwadago kan yajin aiki- ASUU

Published

on

Daga Muhammad Muhammad zahraddin

Shugaban kungiyar malaman Jami’o’i ta ASUU a Najeriya ya ce ba su samu wata sanarwa daga gwamnatin kasar ba kan zama da Ministan Kwadago, da nufin kawo karshen yajin aikin da suke yi.

Advertisement

Shugaban kungiyar Farfesa Emmanuel Osodeke ya fada wa BBC cewa Ministan Kwadago, Chirs Ngige, ne ma ya yi watsi da tattaunawar, ya kuma dakatar musu da albashi da tunanin cewa hakan zai sa su sauya matsayarsu.

A jiya Laraba ne Mista Ngige ya shaida wa manema labarai cewa za su yi wani zama da wakilan ASUU yau Alhamis da nufin kawo karshen tirka-tirkar da ke tsakaninsu, don ganin cewa dalibai sun koma azuzuwansu.

Advertisement

An shafe watanni daliban na zaune a gida, bayan gaza cimma matsaya tsakanin kungiyar malaman jami’o’in da gwamnatin Najeriya.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending