Connect with us

News

YAN SANDA DA YAN KATO DA GORA SUN KASHE MUTUM BIYU A KATSINA

Published

on

Daga Yasir sani Abdullahi

Rundunar Yan sandan jahar KATSINA hadin giwwa da Yan Kato da gora sun dagele Wani hari da Yan ta,adda sukakai garin sabon dawa dake kauyen gundumar safana dake jahar KATSINA

Jaridar daily trust Hausa ta Gambo Isah, mai magana da yawun rundunar ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a jiya Laraba a Katsina.

A cewarsa, lamarin ya afku ne a ranar Talata, 21 ga watan Yuni da misalin karfe biyar na yamma, bayan da aka samu kiran gaggawa cewa ƴan ta’addar da yawansu ɗauke da bindigogi kirar AK-47 sun kai hari kauyen.

“ Da samun rahoton, sai jami’an ‘yan sanda na yankin Safana su ka yi maza su ka mayar da martani bisa jagorancin Babban Jami’in ƴan sanda na safana inda ya ja tawagar ‘yan sanda da ‘yan banga zuwa yankin.

“Daga nan sai suka yi artabu da ‘yan ta’addan da wata muguwar bindiga, inda suka kashe biyu daga cikinsu tare da dakile wannan mummunan aikin nasu,” inji shi.

Advertisement

Isah ya ce kwamishinan ‘yan sanda na jihar, Idrisu Dabban ya yabawa ‘yan sanda, ‘yan kungiyar ƙato-da-gora da jama’ar yankin bisa jajircewarsu wajen kare al’umma daga hare-yan ta adda

 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending