News
Tinubu ya amince ya dauki mataimaki Musulmi – Ganduje
Daga Muhammad Muhammad zahraddin
Ganduje ya na daya daga cikin mutanen da ake hasashen zama mataimakin Tinubu
Gwamanna jihar Kano da ke arewacin Najeriya Abdullahi Umar Ganduje ya ce dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Bola Ahmed Tinubu ya amince zai dauki Musulmi a matsayin mataimakinsa.
Buhari da shuwagabannin tsaro sun gaza, -Ndume.
Ganduje ya yi wannan bayyana haka ne a yayin wata ziyara da manyan malaman jihar kusan 100 suka kai masa ranar Juma’a a gidan gwamnatin jihar.
Gidan talabijin na Channel TV ya ambato gwamnan na cewa ”Mun ba shi shawara ya dauki Musulmi a matsayin mataimaki kuma ya amince, saboda ba wani abu ba ne sabo a Najeriya”.
Ya kumna yi kira ga taron malaman da su rika yi wa Tinubu addu’o’in samun nasara a zaben 2023.
Hakazalika
Gwamnonin APC uku sun ziyarci Wike a Fatakwal
Gwamnoni
Wasu Gwamnonin APC
Wasu gwamnonin jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya sun ziyarci gwamnan Ribas Nyesom Wike a Fatakwal, babban birnin Jihar.
Gwamnonin sun hadar da Kayode Fayemi na Ekiti, da Rotimi Akeredolu na Ondo sai kuma Babajide Sanwo-olu na Legas.
Ko da yake ba su yi bayani kan dalilansu na ziyayar ba, sai dai ba za ta rasa nasaba da kokarin ganin ya fita daga jam’iyyar PDP zuwa APC.
Wike ya sha kaye a hannun tsohon mataimakin shugaban Najeriya Atiku Abubakar a zaben fitar da gwani na dan takarar shugaban kasa a PDP.
Kazalika Atiku ya dauki gwamnan Delta Ifeanyi Okowa a matsayin mataimakinsa, lamarin da wasu ke ganin shi ya sanya ran Wike ya kara baci.
Sai dai jam’iyyar ta PDP ta sha alwashin rarrashinsa ya ci gaba da zama a cikinta.
