Connect with us

News

Gwamnatin jahar Kano ta hana zirga-zirgar baburan Adaidaita sahu daga karfe goma na dare

Published

on

Daga Maryam bashir musa 

 

 

Gwamnatin jihar Kano ta sanar da hana zirga-zirgar babura uku wanda da aka fi sani da A Daidata Sahu bayan karfe 10:00 na dare daga ranar Alhamis 20 ga watan Yuli, 2022.

 

Sanarwar da kwamishinan yada labarai Malam Muhammad Garba ya fitar ta nuna cewa an cimma matsaya kan hakan ne a karshen taron Majalisar tsaro ta jihar Kano.

 

Ya ce matakin wani bangare ne na kokarin tabbatar kare rayuka da dukiyoyin al’umma a jihar.

Advertisement
 

Kwamishinan, a cikin sanarwar, ya bukaci masu tuka baburan masu uku da su bi umarnin, kuma su daina aiki a lokacin da aka kayyade domin jami’an tsaro za su aiwatar da dokar ba tare da wata matsala ba.

 

(Source artv) 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending