News
Gwamnatin jahar Kano ta hana zirga-zirgar baburan Adaidaita sahu daga karfe goma na dare
Daga Maryam bashir musa
Gwamnatin jihar Kano ta sanar da hana zirga-zirgar babura uku wanda da aka fi sani da A Daidata Sahu bayan karfe 10:00 na dare daga ranar Alhamis 20 ga watan Yuli, 2022.
Sanarwar da kwamishinan yada labarai Malam Muhammad Garba ya fitar ta nuna cewa an cimma matsaya kan hakan ne a karshen taron Majalisar tsaro ta jihar Kano.
Ya ce matakin wani bangare ne na kokarin tabbatar kare rayuka da dukiyoyin al’umma a jihar.
Kwamishinan, a cikin sanarwar, ya bukaci masu tuka baburan masu uku da su bi umarnin, kuma su daina aiki a lokacin da aka kayyade domin jami’an tsaro za su aiwatar da dokar ba tare da wata matsala ba.
(Source artv)
-
News2 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
