Connect with us

News

Ƴan fashin daji sun kai hari Zariya sun kuma kashe mutum 4

Published

on

121755241 mediaitem121755240.jpg

Daga Muhammad zahraddin

 

Advertisement

Yan fashin daji sun kai hari kan unguwar Kofar Kona a Zariya ta Jihar Kaduna, inda su ka kashe mutum 4 su ka kuma ji wa da dama rauni.

Majiyoyi sun baiyanawa jaridar DAILY NIGERIAN cewa ƴan ta’addan sun shiga unguwar a ranar Litinin da misalin ƙarfe 10 na dare, in da su ka riƙa harbi kan me-uwa-da-wabi.

Advertisement

An ce bayan harbe-harben, yan bindigar sun kaɗa wani garken shanu cikin jeji.

Jaridar ta ce wani mazaunin yankin, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya ce mazauna unguwar sun yi ta kiran lambar ƴan sanda amma ba a amsa kiran nasu ba.

Advertisement

“mun yi ta kiran lambobin kar-ta-kwana na ƴan sanda amma ba amsa. Sai bayan ma yan bindigar sun ci karensu ba babbaka sannan yan sandan su ka zo.

“Wajen mutum 24 a ka garzaya da su asibitin Gambo Sawaba can a Ƙofar Gayan, in da 4 su ka rasu sakamakon harbin da a ka yi musu da yawa a jikunan su.

Advertisement

“Sun kuma tafi da garken shanu na wasu Fulani sabbin zuwa a yankin,” in ji shi.

Jaridar ta ƙara da cewa Kakakin Rundunar Ƴan Sanda ta Kaduna, Mohammed Jalige bai daga wayar da ta yi masa ba har zuwa lokacin da ta wallafa labarin.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending