Sports
AFCON 2021: Shin ko ka san Alƙaliyar wasa ta farko a gasar cin kofin ƙwallon ƙafa ta Nahiyar Afirka?
Daga Yasir sani Abdullah
Salima Mukansanga, ƴar Ƙasar Ruwanda, ta zamto mace ta farko da ta busa wasa a gasar cin kofin ƙwallon ƙafa ta Nahiyar Afirka.
Duk da cewa a kwai mata huɗu a cikin jagororin wasannin gasar, Mukasanga ta kasance ita kaɗai ce za ta kasance alkaliyar wasa ta tsakiya.
Tuni dai ta busa wasan rukunin B tsakanin Guinea da Malawi.
Advertisements
