Gwamnan Kogi Yahaya Bello ya ayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2023, ƙarƙashin tutar jam’iyyar APC.
Gwamnan ya sanar da matakin ne a wani taron siyasa a Abuja a ranar Asabar.
Da yake jawabi ya yi alƙawalin cewa zai mayar da ƴan Najeriya miliyan biyu masu arziki da za su mallaki miliyoyi nan da 2030.
Ya ce ya fahimci cewa ci gaban Najeriya ya dogara ne da fitar da ƴan ƙasar daga talaucin da ya yi katutu.
