Rahotanni sun ce Saudiyya da Iran sun koma teburin tattaunawa da nufin kyautata alaka tsakanin kasashen biyu da ke gaba da juna.
Kawo yanzu babu wani tabbaci a hukumance, amma wani shafin intanet na yada labarai na gwamnatin Iran ya ce an yi tattaunawar a Bagadaza.
Kasashen biyu na adawa da juna a wasu rikice-rikicen yankin ƙasashen Larabawa da kuma rikicin siyasa.
Sai dai sun fara tattaunawa a bara da nufin rage barazana a yankin.
Iran ta dakatar da tattaunawar a watan da ya gabata ba tare da bayar da wani dalili ba. Matakin ya biyo bayan hukuncin kisa da mahukuntan Saudiyya suka yi wa mutum 81 a rana daya – wanda aka ce rabinsu ‘yan Shi’a ne tsiraru.
