Connect with us

News

2023: Ba za mu yadda da gurbin mataimakin shugaban ƙasa ba — Igbo

Published

on

Daga khadija Abdullahi muhmd 

 

Advertisement

 

Ƙungiyar Ohaneze Ndigbo ta ce ɓangaren inyamirai ba za su yadda a basu gurbin mataimakin shugaban ƙasa a takarar zaɓen 2023 ba.

Advertisement

Ta yi wannan iƙirarin ne a yau Alhamis ta bakin Shugaban ta, Farfesa George Obiozor a taron Imeobi Ohaneze Ndigbo a Enugu.

Ya ce yaƙin neman yankin inyamirai su samu shugaban ƙasa wani yaƙi ne da idan a ka yi masa kallo ma tsanaki za a ga cewa ya dace.

Advertisement

A cewar sa, duk wani batu da kace-nace da a ke yi a kan batun shiyya a na yi ne da niyyar a daƙile ɓangaren inyamirai.

“Sabo da haka ina kira ga duk wasu ƴan takarar shugaban ƙasa daga wannan yankin da su dage, su jajirce su kuma saka imani a zuciyar su.

Advertisement

Obiozor ya kuma bayyana cewa Kwamitin Makomar Siyasar ya kin zai gana da duk wasu masu faɗa a ji a ƙasar nan domin shawo kansu su yarda da dalilan da su ka sanya su ke kiraye-kirayen a baiwa inyamirai mulkin ƙasar nan.

Ya kuma yi kira ga duk wani inyamiri da ya bada goyon baya wajen wannnan yaƙin neman zaɓen.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending