Daga Kabiru basiru fulatan
Gwamnan babban bankin Najeriya ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban ƙasar a zaɓen 2023.
Godwin Emefiele ya ce zai tsaya takarar ne a ƙarƙashin Jam’iyyar APC mai mulki.
Wasu daga cikin waɗanda suka ayyana cewa za su tsaya takara a APC din sun haɗa da mataimakin shugaban Najeriya Yemi Osinbajo da kuma tsohon gwamnan Legas Asiwaju Bola Tinubu.
Jam’iyyun siyasa a Najeriya dai suna da ƙasa da wata guda su tsayar da ɗan takarar shugaban ƙasa
