Connect with us

News

Ganduje Ya Tsayar Da Gawuna a Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano a APC

Published

on

Daga Maryam Bashir musa

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya tsayar da Mataimakin sa, Nasir Yusuf Gawuna a matsayin ɗan takarar gwamnan Kano a jam’iyar APC a zaɓen 2023.

Ganduje ya zaɓi Gawuna ne a wani taron masu ruwa da tsaki da ya gudana.

Advertisement

Majiyoyi makusantan gwamnati sun ce masu ruwa da tsakin kuma sun amince da Kwamishinan Ƙananan Hukumomi, Murtala Sule Garo, ya zama mataimaki a takarar ta Gawuna.

Rahotanni na cewa da ƙyar masu ruwa da tsaki da wasu manya a jihar su ka shawo kan Garo ya amince da yi wa Gawuna mataimaki a takarar.

Advertisement

Ana ganin cewa Garo, a matsayin dan takarar da ya ke da iko da jam’iyar a matakin Kananan Hukumomi, kuma yana samun goyon bayan da mai-ɗakin gwamna.

Wannan matakin baya rasa nasaba da dalilan da yasa jiga jigai daga jam’iyyar ta APC ke sa kafa suna ficewa daga jam’iyyar suna sauya sheka.

Advertisement

Na baya bayan nan shine tsohon kakakin majalisar dokokin jihar Kano, kuma dan majalisar tarayya Rt Hon Alhassan Rurum wanda ya sanar da ficewar sa daga jam’iyyar.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending