News
Ina haɗa aure sama da 300 a shekara — Mai dalilin aure
Daga khadija Abdullahi muhmd
Hajiya Aisha Ahmed, mai sana’ar haɗa aure a Jihar Kano, ta ce ta na haɗa aure har sama da dari uku a shekara.
Ahmed, wacce a ke kira da Mai dalilin aure, ta kuma ce har tsakanin nakasassu ta ke haɗa auratayya.
Da ta ke bayani a wani shiri mai taken Barka da Hantsi a Freedom Radio, wanda Daily Nigerian Hausa ta saurara a yau Laraba, Mai dalilin aure ta ce ana samun wani lokacin matsaloli da har za ta kai ga an fasa aure.
A cewar ta, yawancin matan da ke tuntuɓar ta domin ta nemo musu mazajen aure, sai su ce dole sai mai kuɗi, inda ta ce hakan matsala ce da ke daƙile yin auren a wasu lokuta.
Ta ƙara da cewa suma mazan wani lokacin sai su ce sai mace mai kyau, fara mai gashi, inda ta ce wannan ma ya kan kawo cikas wajen yin auren.
Sannan ta baiyana cewa ta na yin bincike sosai, musamman ɓangaren addini, tarbiyya da sana’a kafin ta haɗa aure.
Sai dai kuma ta ce “mutane da yawa, daga duka ɓangaren mata da mazan, suna yawan kira na su ce in haɗa musu aure. Har da ma masu buƙata ta musamman.
” Duk mai bukata, zai yi mini waya. Daga nan kuma sai na tura musu hotuna ta WhatsApp su zaɓa. Duk wanda ko wacce ta yi, sai a haɗa auren. Kuma alhamdulillah, a na samun nasara domin a shekara ɗaya na kan haɗa aure sama da dari uku,” in ji ta.
-
News4 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News6 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News6 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
