News
EFCC za ta ƙwace jami’ar Nok a Kaduna ta wani ƙusa da ke fuskantar tuhumar rashawa a Najeriya
Daga Usman Abdullahi jibirin
Wata Kotu a Najeriya ta umarci hukumar yaƙi da rashawa ta EFCC ta ƙwace jami’ar Nok mai zaman kanta mallaki wani tsohon babban jami’in gwamnati da ke fuskantar tuhuma kan Rashawa.
EFCC ta ce, Anthony Hassan, wanda tsohon darakta ne na harkokin kuɗaɗe a ma’aikatar lafiya, ya gina jami’ar ne da kuɗin Rashawa.
Sai dai wani abu da ba a fayyace ba, shi ne ko matakin zai shafi karatun ɗalibai a makarantar da ke arewacin Kaduna.
Kuma babu wasu karin bayyanai kan ko Mista Hassan zai ɗaukaka ƙara.
Sannan baya ga ƙwace jami’ar, akwai kadarorinsa da otel din alfarma da aka umarci a karɓe su.
A ‘yan kwanakin nan dai EFCC ta buɗe wuta kan binciken Rashawa a faɗin ƙasar.
-
News3 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News3 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
