News
An tantance mai rajin kare shan wiwi a matsayin ɗan takarar shugaban kasa a Kenya
Daga Muhammad Muhammad zahraddin
An tantance wani dan siyasa da ke rajin kare shan tabar wiwi a Kenya, a matsayin dan takarar shugabancin kasar a zaben da za a yi a watan Agusta mai zuwa.
George Wajackoyah, wani lauya kuma Farfesa ya yi kokarin samun aikin ba tare da yin wani aiki sosai ba.
Amma a wannan karon, abin da ya sa a gaba a yakin neman zabe, na tabbatar da shan wiwi ya janyo masa goyon baya tun bayan kaddamar da takararsa a watan Fabirairu.
Ya kafa wata jam’iyyar siyasa da ake kira Roots da take son Kenya ta bari a rika sha da noman wiwi inda zai taimaka a biya bashin da ake bin kasar mai dinbin yawa.
A farkon wannan makon ne, aka yi watsi da yunkurinsa na takara saboda bai cika sharudan da ya kamata.
A ranar Alhamis kuma ya kara mayar da takardunsa inda aka tabbatar da takararsa saboda cika sharudan da aka shimfida.
-
News3 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News3 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
