News
ajin Aiki: ASUU Ta Lashi Takobin Hukunta Jami’o’in Da Suka Bijire Mata
Daga khadija Abdullahi muhmd
Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta yi barazanar daukar mataki kan duk jami’ar da ta yi kunnen uwar shegu da umarnin da ta bayar na ci gaba da yajin aiki, yayin da take tattaunawa da gwamnati kan bukatunta.
Za a ƙara samun hauhawar farashi da rashin wuta da abinci da fetur a Najeriya – Bankin Duniya
Shugaban Kungiyar na kasa, Farfesa Osodeke ne ya bayyana hakan ga manema labarai Abuja, in da ya ce za su tabbatar da daukar mataki kan wadanda suka yi biris da umarnin kungiyar.
Shugaban ya ce tuni ma sun riga sun fara aika takardar neman bahasi ga wadanda suka aikata hakan kamar dai yadda yake a dokar kungiyar.
Ya kuma ce tun lokacin da kungiyar ta zauna a taron tattaunawar da Shugaban Ma’aikata ya kira su kimanin wata guda da ya gabata, gwamnati ba ta sake tuntubar su ba, sai dai ya ce za su sake shiga wani taron tattaunawar nan da sati guda.
Idan za a iya tunawa, kimanin wata biyar ke nan kungiyar ta shafe tana gudanar da yajin aiki, bisa kin biya mata bukatunta, da kuma cika musu alkawuran da gwamnati tayi tun a 2009.
Aminya dai ta gano cewa wasu daga cikin jami’o’in kasar nan irinsu Ladoke Akintola (LAUTECH) da ke Ibadan tuni sun koma bakin aiki duk da umarnin kungiyar.
-
News2 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
