Wani jirgin sama na kamfanin Jubba Airways ya fadi a lokacin da yake kokarin sauka a filin saukar jiragen sama na magadishu babban birnin Somaliya.
Hukumomi sun ce an samu nasarar kubutar da duka fasinjoji da ma’aikatan jirgin 30 da ke cikin jirgin.
Rikicin Hausawa Da ’Yan Kabilar Brita Ya Kashe Gommai A Sudan
Hotunan da gidan tabijin na SNTV mallakar gwamnatin kasar ya wallafa a shafinsa na tuwita sun nuna yadda ma’aikatan bayar da taimakon gaggawa na filin jirgin ke kokarin kashe wutar da ta kama jirgin bayan an kubutar da fasinjojin.
