Connect with us

News

Yan Sandan Da Ke Karbar Na-Goro Sun Ba Ni Kunya —Alkali Baba

Published

on

Police

Daga Yasir sani Abdullahar.

Sufeto-Janar na ‘Yan Sandan Najeriya, IGP Usman Alkali Baba, ya bayyana cewa jami’an da ke karbar na-goro sun ba shi kunya.

Advertisement

Alkali Baba ya bayyana takaicinsa kan yadda aka samu wasu jami’an ‘yan sanda da muzguna wa jama’a, musamman masu karbar na-goro.

Don haka ya bukaci dukkan Kwamishinoni da Kwamandojin ‘yan sanda da su mai da hankali sosai wajen sanya wa jami’ansu ido yadda ya kamata.

Advertisement

A cewar Mai Magana da Yawun Rundunar ‘Yan Sanda, CSP Olumuyiwa Adejobi, Baba ya yi gargadin rundunar ba za ta lamunci halin muzgunawa da kuma karbe sulalan jama’a da wasu jama’ai ke yi ba.

Kazalika, ya bai wa Maitaimakin Sufeto-Janar (AIG) na sashen tattara bayanan sirri, umarnin sanya ido kan wasu rassa uku na rundunar wajen tabbatar da suna aikinsu yadda ya kamata ba tare da take hakkin jama’a ba.

Advertisement

Ya ce an dauki wannan mataki ne domin tabbatar da sassan rundunan sun cimma manufofinsu na aiki.

Rahotanni sun ce Alkali Baba ya ba da sanarwar korar Liyomo Okoi, wani jami’in dan sanda mai mukamin Kwanstebul da lambar aiki 524503.

Advertisement

Sanarwar ta ce an kori Okoi da ke Ofishin Ekori a Kuros Riba, daga aiki bayan da aka kama shi da rashin da’a kamar yadda wani bidiyonsa da aka nada ya nuna.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending