News
Mutum 7 Sun Rasu Bayan Rushewar Gini A Jigawa
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Wasu mutum bakwai sun rasu a safiyar Asabar sakamakon rushewar gini a Karamar Hukumar Birniwa ta Jihar Jigawa.
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Jiagawa ta ce mutanen sun rasu ne nan take bayan ginin ya rufta a kansu da misalin karfe 5:47 na asuba a kauyen Bursali.
Wani dan kasar China ya kashe wata budurwa a Kano
Kakakin Rundunar, DSP Lawan Shiisu Adam, ya kara da cewa wani mutum daya ya jikkata sakamakon rushewar ginin.
Ya ce ’yan sanda sun garzaya da su zuwa Babban Asibitin Birniwa, inda likitoci suka tabbatar da rasuwar mutum bakwai din, na takwas din kuma yake samun kulawa.
Ya kuma bayyana cewa ginin da ya yi ajalin mutanen an yi shi ne da kasa.
DAILY TRUST
-
News5 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Cafke Mai Safarar Makamai, Sun Kwato Harsasai 637 A Kaduna
-
News7 days ago
Jami’an NSCDC Sun Cafke Mutane Biyu Da Saniyar Da Ake Zargin Ta Sata Ce A Kano
-
News4 days ago
2027: INEC Ta Tabbatar Da Ibrahim Ali Amin Little A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano A Jam’iyyar ADC
