News
Akwai Fargabar Rasa Rai Tare Da Jikkatar Su Yayin Rushewar Gini A Jigawa
Mutum ɗaya ya rasu, yayin da wasu bakwai suka jikkata a wani mummunan hatsari na rugujewar gini da aka tattaro cewa ruwan sama ya haddasa, a ƙauyen Kabak da ke ƙaramar hukumar Kirikasamma, jihar Jigawa.
Jami’in yaɗa labarai na ƙaramar hukumar, Musa Muhammad, ya tabbatar da aukuwar lamarin, inda ya ce mutum biyar na kwance a asibiti suna samun kulawa, yayin da aka sallami biyu bayan an yi musu magani.
Shugaban ƙaramar hukumar, Muhammad Maji, ya kai ziyarar jaje ga iyalan da abin ya shafa tare da bayar da tallafin kuɗi ga waɗanda suka jikkata da kuma dangin mamacin.
Lamarin ya faru ne a daidai lokacin da ake cigaba da samun rahotannin rushewar gine-gine a sassa daban-daban na ƙasar, musamman manyan biranen Abuja da Legas, abin da ke ƙara janyo damuwa kan ingancin gine-gine a Najeriya.
