News
Za A Kafa Hukumar Kula Da Magunguna A Filato
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Gwamnan Filatu Simon Lalong ya sanya hannu kan kudirin sabuwar dokar samar da Hukumar Kula da Magunguna a jihar.
Gwamnan ya sanya hannu kan kudirin dokar mai sashi 11, da kananan sassa 52 a Fadar Gwamnatin Jihar da ke Jos, a ranar Alhamis.
An tafka muhawara tsakanin masu takarar kujerar gwamna a Kano
Aminiya ta rawaito cewa Bayan sanya hannun ne kuma, ya ce dokar ba karamin alfanu za ta kawo ga rayuwar al’ummar jihar ba.
“In dai aka dabbaka dokar kamar yadda aka tsara ta, za ta saukaka wa al’umma samun magunguna masu inganci da rahusa a asibitocin jihar da na manyan makarantu, hadi da na duba gari,” in ji gwamnan.
Ya kuma gode wa ’yan Majalisar Dokokin jihar, bisa gaggawar mayar da hanakali kan kudirin, da kuma gaggauta zartar da dokar.
