Sports
Sadio Mane ya ji rauni a wasan da Bayern ta Lallasa Weder Bremen
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Raunin da Sadio Mane ya ji ne ya mamaye nasarar lallasa Werder Bremen da Bayern Munich suka yi 6-1 a wasan Bundesliga, abin da ya kai su saman teburin gasar da ratar maki 4.
Mane ya bukaci kulawa ta kwararru bayan da fadi a minti na 15 da fara wasa har sai da aka maye gurbinsa da Leroy Sane.
EFCC Ta Daukaka Kara Kan Hukuncin Aike Da Shugabanta Gidan Yari
Wannan na zuwa ne ana saura kwanaki 13 kacal Senegal su buga wasansu na farko a gasar cin kofin duniya ta shekarar 2022 da Netherlands a Qatar.
Sai dai Bayern sun samu nasara a wasan duk da haka, inda Serge Gnabry ya ci kwallaye 3 rigis.
Mane wanda sau biyu yana lashe kyautar gwarzon dan kwallon kafar Afrika, dan wasa ne mai mahimmanci a tawagar kwallon kafar Senegal, wadda za ta fafata da tawagar Holland a wasan farko na rukunin A na gasar kofin duniya a ranar 21 ga watan Nuwamba.
