Connect with us

News

NPC Ta Sha Alwashin Gudanar Da Sahihiyar Kidaya A 2023

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Hukumar kidaya ta kasa (NPC) ta sha alwashin gudanar da sahihin kidayar mutane da gidaje a fadin Nijeriya a 2023.

 

Advertisement

Kwamishinan hukumar NPC a Jihar Katsina, Injiniya Bala Almu Banye ya bayyana haka a lokacin taron manema labarai dangane da bude shafin yanar gizo na daukar ma’aikatan da za su gudanar da aikin kidayar.

INEC ta fara kafe rajistar sunayen masu kaɗa ƙuri’a a faɗin Najeriya

Ya yi nuni da cewa bin hanyar zamani wajen daukar ma’aikatan kidayar wani bangare ne na kudurin hukumar na gudanar da sahihi kuma ingantacciyar kidaya.

Advertisement

 

Injiniya Almu ya kara da cewa yawan ma’aikatan kidayar da za a dauka ya danganta da yawan yankuna da ke fadin kasar nan.

Advertisement

 

Ya ce hukumar ta kafa tawagar daukar ma’aikatan kidayar na kananan hukumomi da na jiha domin tabbatar da ganin an dauko mutanen da ke yankunan don gudanar da aikin.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Kwamishinan hukumar ya ce ma’aikatan da ake bukatar dauka sun hada da masu bayanai, jami’an bayar da horo, masu duba aiki, masu daukar bayanai da dai sauransu.

Advertisement

Ya bayyana cewa daga cikin ka’idojin yin rijistar ma’aikatan akwai lambar NIN da ta asusun ajiya na banki.

 

Advertisement

Ya kara da cewa shafin daukar ma’aikatan kidayar zai ci gaba da zama a bude har zuwa watan Disamba, amma za a rufe shi na wani lokaci tsakanin ranakun 7 zuwa 13 ga wannan watan na Nuwamba.

 

Advertisement

Kwamishinan ya shawarci masu neman aikin su yi taka tsan-tsan don kar su tura bayanai ba daidai ba.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending