Connect with us

News

Kuɗaɗen sata da muka ƙwato sun kai dala biliyan ɗaya – Gwamnatin Najeriya

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce ta gano tare da ƙwato dala biliyan ɗaya da aka sace sakamakon bincikar kuɗin sata da gwamnatin mulkin shugaba Buhari ke yi tun farkon hawansa zuwa yau.

Advertisement

 

Ministan Shari’a na ƙasar Abubakar Malami ne ya bayyana haka ga manema labarai a fadar shugaban ƙasar, bayan kammala taron majalisar zartarwar ƙasar da ake gudanarwa mako-mako, wanda shugaban ƙasar Muhammadu Buhari ya jagoranta.

Advertisement

Miliyoyin mutane sun yi asara yayin da gobara ta tashi a kasuwar Delta

Malami ya tabbatar da cewa ƙudin da aka ƙwato an zuba su a fannoni daban-daban na tattalin arzikin ƙasar cikin har da shiri gwamnati ƙasar na yaƙi da talauci.

 

Advertisement

Haka kuma ministan ya bayyana damuwar gwamnati kan cushe a kasafin ƙudin ƙasar, ya ce hakan abin takaici ne, ya kuma ƙara da cewa za a ɗauki ƙwaƙƙwaran mataki domin magance hakan.

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending