Sports
Manyan lig-lig na duniya za su karrama Pele
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Manyan lig lig na duniya sun bayyana shirinsu na karrama Pele — wanda galibi a duniyar kwallon kafa ake kallon a matsayin gwarzon da ba a taba ganin irinsa ba — wanda kuma ya mutu a Brazil ranar Alhamis.
Za a yi tafi na tsawon minti daya kafin buga wasannin gasar Premier ta Ingila, kuma ‘yan wasa za su ɗaura bakar damara a hannu.
Haka ma a gasar La Liga ta Spain za a yi shiru na minti daya don karrama Pele – wanda shi ne mutum daya tilo da ya lashe kofin duniya sau uku.
Hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA — ta sassauta dukkanin tutoci a hedkwatarta da ke Zurich.
Brazil ta ayyana kwanaki uku na zaman makoki.
Advertisements
