Connect with us

News

Gwamnatin Tarrayya Ta Musanta Shirin Soke NBAIS

Published

on

FB IMG 1762488671790 768x511

Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya ta karyata rahotannin da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa Gwamnatin Tarayya da Majalisar Dokoki ta Kasa na shirin soke Hukumar Kula da Jarabawar Larabci da Ilimin Addinin Musulunci ta Kasa (NBAIS).

A cikin wata sanarwa da Daraktar Yada Labarai da Hulda da Jama’a ta ma’aikatar, Folasade Boriowo, ta fitar a ranar Laraba a Abuja, ta bayyana cewa ikirarin ba gaskiya ba ne, kuma babu wata hujja da ke nuna hakan.

Advertisement

Ƙungiyar Tsofaffin Dalibai Ta Nemi A Gaggauta Sake Buɗe Unity College Karaye Aka Rufe Sama Da Shekaru Uku

Ta ce ma’aikatar ba ta gabatar da wata doka a gaban Majalisar Dokoki ta Kasa domin soke NBAIS ba, kuma ba ta amince da wata manufa da za ta tauye ayyukan hukumar ba.

Advertisement

Boriowo ta yi gargadin cewa irin wannan bayanan ƙarya na iya haifar da fargaba da rudani a tsakanin ɗalibai, iyaye, malamai, ƙungiyoyin addini da sauran masu ruwa da tsaki.

Ta jaddada cewa NBAIS har yanzu hukuma ce da gwamnatin Najeriya ta amince da ita wajen gudanar da jarabawa da bayar da takardun shaida a cikin tsarin ilimin ƙasar.

Advertisement

Ma’aikatar ta kuma tabbatar da cewa gwamnatin tarayya za ta ci gaba da tallafa wa dukkan hukumomin ilimi da aka kafa bisa doka, tare da bin manufofin ilimi na ƙasa da ka’idojin adalci da bai wa kowa dama iri ɗaya.

A ƙarshe, ma’aikatar ta bukaci jama’a da su yi watsi da rahoton, tare da neman su rika dogaro da sahihan bayanai daga hukumomin gwamnati domin samun ingantattun bayanai kan manufofi da sauye-sauyen da suka shafi ilimi.

Advertisement

 

 

Advertisement

DAILY NIGERIAN 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending