Connect with us

Sports

Ronaldo ya yi saɓul-da-baka a Saudiyya

Published

on

Cristiano Ronaldo

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

 

Advertisement

 

Shahararren ɗan ƙwallon ƙafar duniya Cristiano Ronaldo ya yi tuntuɓen harshe a lokacin da ake gabatar da shi ga sabuwar ƙungiyar da ya koma ta Al Nassr ranar Talata,

Advertisement

 

Ronaldo ya yi suɓul-da-baka a gaban magoya bayan ƙungiyar inda ya ce ‘South Afirka’ a maimakon ‘Saudi Arabiya’.

Advertisement

Sama da mutum miliyan shida ba su karɓi katin zaɓensu ba – INEC

Ɗan wasan ya koma Al Nassr ranar Juma’a bayan da ya raba-gari da tsohuwar ƙungiyarsa Manchester United.

 

Advertisement

Ronaldo ya ce: “Wasan ƙwallon ƙafa wani abu ne na daban, dan haka zuwana ‘South Afrika’ ba shi ne ke nuna cewa ta-ƙare min ba”

 

Advertisement

”Wannan shi ne dalilin da ya sa nake son samun sauyi, haƙiƙa ban damu da abin da mutane ke cewa ba”, kamar yadda Ronaldo ya bayyana wa manema labarai a lokacin da aka gabatar da shi a birnin Riyadh.

 

Advertisement

Ya ƙara da cewa: “Na samu komai, na yi wasa a manyan ƙungiyoyi a Turai, a yanzu kuma lokacin buɗe sabon babi ne a Asiya”.

 

Advertisement

Bayan taron manema labaran, ɗan wasan ya sanya sabuwar rigar wasansa ta ƙungiyar a filin wasan a gaban dubban magoya bayanta.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending