Sports
PSG Za Ta Tsawaita kwantiragin Messi
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Kungiyar Paris Saint Germain ta shiga tattaunawar tsawaita kwantiragin fitaccen dan wasanta Lionel Messi na Argentina.
Luis Campos, mai ba da shawara kan harkokin kwallon kafa na PSG ne ya tabbatar a wannan Lahadin.
A halin yanzu dai yarjejeniyar Messi za ta kare a watan Yunin 2023.
Shugabannin PSG sun bayyana fatan Messi zai ci gaba da zama a kungiyar duk da cewa suna cikin tattaunawa.
Dan wasan mai shekara 35 wanda kuma ya lashe kyautar Ballon d’Or sau bakwai dole ne ya yanke shawarar abin da makomarsa za ta kasance.
Lamarin dai na zuwa ne ’yan makonni bayan ya kai ga lashe Gasar Kofin Duniya ta 2022 a Qatar.
A shekarar 2021 ce Messi ya sauya sheka zuwa PSG kan yarjejeniyar shekaru biyu, bayan ya shafe tsawon shekaru a Barcelona.
-
News4 days ago
Ban Taɓa Nadamar Adawa Da Yunƙurin Obasanjo Na Wa’adin Mulki Karo Na Uku Ba — Atiku
-
News4 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Ƙwato Na’urorin Solar 160 Da Darajarsu Ta Kai Kimanin Naira 59.2 A Kano
-
News2 days ago
Wasu Kansiloli Na Zargin Ciyaman Da Daukar ‘Yan Daba Domin Kai Musu Hari A Kano
