Sports
PSG Za Ta Tsawaita kwantiragin Messi
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Kungiyar Paris Saint Germain ta shiga tattaunawar tsawaita kwantiragin fitaccen dan wasanta Lionel Messi na Argentina.
Luis Campos, mai ba da shawara kan harkokin kwallon kafa na PSG ne ya tabbatar a wannan Lahadin.
A halin yanzu dai yarjejeniyar Messi za ta kare a watan Yunin 2023.
Shugabannin PSG sun bayyana fatan Messi zai ci gaba da zama a kungiyar duk da cewa suna cikin tattaunawa.
Dan wasan mai shekara 35 wanda kuma ya lashe kyautar Ballon d’Or sau bakwai dole ne ya yanke shawarar abin da makomarsa za ta kasance.
Lamarin dai na zuwa ne ’yan makonni bayan ya kai ga lashe Gasar Kofin Duniya ta 2022 a Qatar.
A shekarar 2021 ce Messi ya sauya sheka zuwa PSG kan yarjejeniyar shekaru biyu, bayan ya shafe tsawon shekaru a Barcelona.
-
News5 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News1 day ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
