News
Najeriya na bincike kan zargin biyan miliyoyin kuɗi don yi wa ‘yan sanda ƙarin girma.
Hukumar kula da aikin ‘yan sanda a Najeriya ta ce ta kafa kwamitin bincike don bin diddigin zargin cewa ana biyan sama da naira miliyan bakwai kafin a yi wa manyan jami’an ‘yan sanda ƙarin girma.
Hukumar ta yi kira ga duk wani da ke da wata shaida kan wannan zargi, ya bayyana gaban ta, don gudanar da bincike.
Wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Ikechukwu Ani ya fitar ta ce matakan, martani ne kan wani rahoto da wata jaridar intanet a Najeriya ta buga mai taken ‘badaƙalar cin hanci ta tashi hankula a hukumar kula da aikin ‘yan sanda’.
Rahoton ya yi zargin cewa sai an biya cin hancin $10,000, kimanin naira miliyan bakwai, kafin a yi wa manyan ‘yan sanda ƙarin girma a hukumar.
Ta dai yi alƙawarin ɗaukar mataki a kan duk jami’in da aka samu da hannu kan zargin karɓar cin hancin.
Kwamitin a cewar sanarwar Mista Ani, ya ƙunshi jami’an rundunar ‘yan sanda da kuma na hukumar kula da aikin ‘yan sanda.
-
News4 days agoWasu Ƴan Daba Sun Kai Farmaki Kasuwar Siyar Da Wayoyi Ta Farm Center Dake Kano
-
News6 days agoWasu Fusatattun Matasa Sun Ƙona Mutum Uku Har lahira A Filato
-
News6 days agoAbin Takaici Ne A Kyale Mata Su Cire Wandunan Da Aka Basu Akan Titi Suna Dagawa A Cikin Al’ummar Da Ke Alfahari Da Kunya Da Addini
