News
Tinubu Ya Janye Sunan Maryam Shetty Daga Sunayen Ministocinsa
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN.
Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya janye sunan Dr Maryam Shetty amatsayin minista daga jihar Kano.
Umarnin na Tinubu na kunshe ne a cikin wata wasika da shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio ya karanta a zauren majalisar yau Juma’a.
‘yan bindiga sun kashe ‘ya’yan jami’in ‘yan sanda biyu, tare da raunata matarsa a jahar Jigawa
A cewar wasikar, Mariya Mahmud ce za ta maye gurbin Dr Shetty a matsayin na minista.
Shugaban kasar ya kuma bayyana Festus Keyamo SAN a matsayin wanda ya nada a matsayin minista.
Bisa wannan kari a yanzu adadin wadanda aka nada a matsayin ministoci ya karu zuwa 48.
Advertisements
