News
Hukumar NDLEA Ta Kama Miyagun Kwayoyi Masu Nauyin Kilogram 100,458 A Jihar Kaduna
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA reshen jihar Kaduna, ta kama miyagun kwayoyi masu nauyin kilogram dubu 1 dari 458 a cikin watan Disamba.
Wannan dai na kunshe cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar a yau Talata dauke da sa hannun jami’in yada labarai na hukumar Sha’aibu Omale.
Harin Yan Bindiga Da Ya Faru A Filato Babban Abin Tashin Hankali Ne -Shehu Sani
Omale, yace abubuwan da hukumar ta kama sun hada da kwayoyin tiramadol da koken da sauran miyagun kwayoyi. Hakalika mai magana da yawun hukumar yace an damke wasu mutane 103 da ake zargi da alaka da ta’ammali da miyagun kwayoyi.
A wani labarin kuma Harin Yan Bindiga Da Ya Faru A Filato Babban Abin Tashin Hankali Ne -Shehu Sani
Babban Bankin Najeriya CBN ya sauya matsayarsa kan hada-hada da kuɗin intanet ko kuma cryptocurrency a ƙasar.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito wata sanarwa da bankin ya fitar ranar Juma’a da ke umartar bankunan kasuwanci na Najeriya cewa su yi watsi da haramcin da ya saka kan amfani da kuɗin na crypto tu a 2021.
CBN ya ce yadda ake yayin kuɗin na crypto yanzu a faɗin duniya ya nuna irin buƙatar da ake da ita ta saka dokoki a kan sa.
“A watan Fabarairun 2021 CBN ya haramta wa bankuna da sauran cibiyoyin kuɗi amfani da cryptocurrency saboda almundahanar kuɗi da kuma ɗaukar nauyin ta’addanci,” in ji sanarwar.
“Sai dai kuma, abin da ke faruwa a duniya ya nuna cewa akwai buƙatar a kula da dukiyoyin hada-hada ta intanet wato Virtual Assets Service Providers (V/ASPs).”
Ya ƙara da cewa hukumar kula da hada-hada da hannayen jari za ta fitar dokoki da sharuɗɗan amfani da dukiyoyoin intanet ɗin.
Amma babban bankin ya jaddada haramcin yin kasuwanci, ko kuma mallakar asusun crypto ga bankunan kasuwancin su da kansu
-
News3 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
