Connect with us

News

Harin Yan Bindiga  Da Ya Faru A Filato Babban Abin Tashin Hankali Ne -Shehu Sani

Published

on

Tsohon Sanata mai wakiltar jahar Kaduna ta tsakiya a majalisar dattawan Nijeriya Sanata Shehu Sani

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN

Tsohon Sanata mai wakiltar jahar Kaduna ta tsakiya a majalisar dattawan Nijeriya Sanata Shehu Sani ya mayar da martani kan wasu munanan abubuwan da suka faru a jihar Filato a jajibirin Kirsimeti.

Yan bindiga dai sun kai hare-hare a lokaci guda kan al’umma sama da goma sha biyar a kananan hukumomin Bokkos da Barkin-Ladi na jihar a jajibirin Kirsimeti.

Kungiyar Manyan Likitocin Dabbobi Tayi Allah Wadai Da Kashe Wasu Kananan Giwaye Da Aka Yi A Borno

‘Yan ta’addan sun kona gidaje daban-daban a daren Lahadi, sannan sun yi awon gaba da kayan gona tare da lalata dukiyoyi yayin da suke yanka mutanen.

Daily Post ta ruwaito cewa Gwamnan jihar Filato, Caleb Mutfwang, a ranar Talata, ya bayyana a gidan talabijin na Channels Television’s Sunrise Daily cewa adadin wadanda suka mutu a harin jajibirin Kirsimeti a jihar ya haura 115.

Sai dai da yake magana kan lamarin, Sani, a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter a ranar Talata, ya ce ya kalli bidiyon sakamakon kisan gillar da aka yi a Filato, inda ya kara da cewa inda wani jariri ke kuka a bayan gawar mahaifiyarsa ne yafi tayar da hankali.

Advertisement

Ya kuma bayyana wannan lamari mai cike da bakin ciki a matsayin daya daga cikin munanan ayyukan ta’addancin da ya taba gani.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending