News
Kungiyar Manyan Likitocin Dabbobi Tayi Allah Wadai Da Kashe Wasu Kananan Giwaye Da Aka Yi A Borno
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Kungiyar manyan likitocin dabbobi ta kasa tayi Allah wadai da kashe wasu kananan giwaye da aka yi a karamar hukumar Kala Balge dake jihar Borno.
Haka nan kungiyar ta nuna damuwa kan yadda aka kashe wasu shaho guda biyu a yankin jihohin Kebbi da Sakwwato wadanda suka yi hijira daga yankin Turai.
Shugaban kungiyar na kasa Dr. Moses Akoroyo, shine ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a Abuja.
Sawaba radiyo ta ruwaito cewa Yace abin takaici ne yadda aka nuna wani faifan bidiyo a shafin sada zumunta na yadda wasu jami’an soji suka hallaka wasu giwaye.
Moses, ya kara da cewa kungiyar tana sanar da sauran abokan aikinta da hukumomin kula da Gandun daji cewa suna sane da wannan labarin. Kazalika shugaban kungiyar yace za su hada kai da sauran masu ruwa da tsaki domin dakile wannan al’amari na kashe dabbobin daji dake neman zama ruwan dare.
A Wani labarin kuma Mai Binciken CBN ya gayyaci Tunde da wasu mutum biyu
Babban Bankin Najeriya CBN ya sauya matsayarsa kan hada-hada da kuɗin intanet ko kuma cryptocurrency a ƙasar.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito wata sanarwa da bankin ya fitar ranar Juma’a da ke umartar bankunan kasuwanci na Najeriya cewa su yi watsi da haramcin da ya saka kan amfani da kuɗin na crypto tu a 2021.
CBN ya ce yadda ake yayin kuɗin na crypto yanzu a faɗin duniya ya nuna irin buƙatar da ake da ita ta saka dokoki a kan sa.
“A watan Fabarairun 2021 CBN ya haramta wa bankuna da sauran cibiyoyin kuɗi amfani da cryptocurrency saboda almundahanar kuɗi da kuma ɗaukar nauyin ta’addanci,” in ji sanarwar.
“Sai dai kuma, abin da ke faruwa a duniya ya nuna cewa akwai buƙatar a kula da dukiyoyin hada-hada ta intanet wato Virtual Assets Service Providers (V/ASPs).”
Ya ƙara da cewa hukumar kula da hada-hada da hannayen jari za ta fitar dokoki da sharuɗɗan amfani da dukiyoyoin intanet ɗin.
Amma babban bankin ya jaddada haramcin yin kasuwanci, ko kuma mallakar asusun crypto ga bankunan kasuwancin su da kansu
-
News3 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion6 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News3 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
