Connect with us

News

Mutum 12 Sun Mutu, 28 Sun Jikkata A Wani Hadarin Mota A Hanyar zariya Zuwa Kano 

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

Mista Kabir Nadabo, Kwamandan hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC) na jihar Kaduna, ya ce akalla mutane 12 ne suka mutu sannan 28 suka samu raunuka a wani hadarin mota da ya rutsa da su a hanyar Zariya zuwa Kano.

Nadabo ya shaidawa Kamfanin Dillancin Labarai Na Kasa NAN a ranar Litinin a Kaduna cewa, hatsarin motan ya yi sanadiyar rayuka a kauyen Tashar Yari da karfe 7:36 na safiyar ranar Litinin.

Nikki Haley ta kayar da Trump a zaben fitar da gwani a Washington

“Tirelar mai lamba KTG 454 ZZ tana kan hanyar zuwa Kano lokacin da lamarin ya faru,” in ji Nadabo.

Ya ce abin da ya haddasa hatsarin ya faru ne bisa kuskure,da Kuma wuce gona da iri .

Ya ce binciken da aka gudanar ya nuna cewa mutane 40 ne suka samu hatsarin, 28 sun samu raunuka, 12 kuma sun mutu.

Advertisement

Daily News24 ta ruwaito cewa An kai wadanda suka jikkata zuwa babban asibitin Makarfi domin ci gaba da kula da su.

 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending