Connect with us

News

Sanusi ya ɓarke da kuka a lokacin da yake jawabin ta’aziyyar rasuwar Herbert Wigwe

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI  

Tsohon Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya fashe da kuka a lokacin da ya ke jawabi a wurin taron karrama marigayi Herbert

Wigwe, tsohon shugaban rukunin kamfanin Access Holdings Plc.

Majalisar wakila ta yi yunkurin  kara yawan tarar da ake ci kan wadanda aka samu da lefin wulakanta Tutar Najeriya

Da yake jawabi ga dimbin jama’ar da suka halarci tron bikin karrama marigayin mai shekaru 57, tsohon Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN) Sarki Sanusi ya ce ya yi zaton zai riga Herbert mutuwa.

” A nawa lissafin na yi zaton zan riga Herbert mutuwa, amma sai gashi ya tafi ya barmu a duniya.

Bayan haka da sarki Sanusi ya bayyana yadda marigayi Herbert ya tsaya masa tsayin daka a lokacin da gwamnatin Kano ta rantse sai ta ga bayan sa a sarautar Kano.

Advertisement

” A lokacin da na tabbatar ba makawa sai za a cire ni daga sarautar Kano, na kira shi na ce masa, Herbert, sai dai fa ayi hakuri amma babu makawa za a tsige ni daga sarautar Kano.

” A lokacin da aka sanar da tsige ni, da karfe tara na safe kafin 12 na rana, ya aiko da jirgin sama, na saka iyalaina zuwa Legas.

” Da suka sauka Legas, ya ajiye a Otelsaga baya kuma ya saka su a gida. Ya ce min duk abinda nake so yana nan tare da kai.

Bayan haka Sarki Sanusi ya bayyana yadda Herbert ya taimaka masa kan harkokin kuɗaɗensa na ajiya da na asusun ƴaƴan sa na karatu da sauransu.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending